Politics

Ƴan Kwankwasiyya sun yi dandazo a wajen zaben shugabannin jam’iyar NNPP a Kano

Ƴan Kwankwasiyya sun yi dandazo a wajen zaben shugabannin jam’iyar NNPP a Kano

Dubban yan Kwankwasiyya ne suka mamaye harabar wurin da Jam’iyyar NNPP Mai kayan marmari za ta gudanar da baban zabenta.

Daily Nigerian Hausa ta gano cewa an tsara gudanar da zaben ne a cibiyar koyar da Sana’o’i ta sani Abacha wato Abacha Youth Center da ke kan hayar Madobi.

Ana sa ran Jam’iyyar za ta zabi shugabaninta a mataki daban daban ayau Litinin.

Sai dai abinda ke jan hankali a wurin taron shi ne yadda magoya bayan Kwankwasiyya suka mamaye wurin.

Wannan dai baya rasa nasaba da yadda ake ta rade-radin jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso zai koma cikin Jam’iyyar zuwa nan da ƙarshen watan Maris.

Idan za a iya tunawa dai tun a watan da ya gabata ne Jam’iyyar ta rushe shugabancinta, tare da kafa kwamitin riko.

A yau Litinin ne dai a ke gudanar da zaben shugabannin Jam’iyyar da kuma ake ganin yan Kwankwasiyya ne suka mamaye dukkanin mukaman da za a zaba.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button