E/News

Mai shigar da ƙara a Kotun Duniya ya nemi a kama Netanyahu da shugabannin Hamas

Babban mai shigar da ƙara na Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) ya nemi kotun ta ba da umarnin kama Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da kuma jagoran Hamas a Gaza saboda aikata laifukan yaƙi.

Karim Khan ya ce akwai hujjoji ƙarara da ke tabbatar da cewa ɓangarorin biyu sun aikata laifukan yaƙi da na tarwatsa rayuwar ɗan’adam daga ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

Kotun ta ICC da ke birnin Hague na bincikar ayyukan Isra’ila a yankunan Falasiɗnawa da ta mamaye tun daga shekara uku da suka wuce – da kuma ayyukan Hamas a baya-bayan nan.

Mista Netanyahu ya siffanta ba da umarnin kama shugabannin Isra’ila da ICC za ta yi a matsayin “abin takaici da zai jawo matsala a tsawon tarihi”.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button