![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2023/05/Capture-2023-05-05-22.10.57.jpg?resize=780%2C470&ssl=1)
Rundura ƴan sanda a jihar Kano sun sanar da kama matashin nan Ibrahim Musa da ake zargi ya kashe mahaifiyarsa a Kano.
Kiyawa ya ce matashin ya amsa laifin da ake zarginsa da shi, inda kuma ya ce yana tu’ammali da ƙwayoyi masu sa maye.
A yanzu dai za a tura shi zuwa kotu bayan kammala bincike.
A jiya ne dai aka ruwaito cewa matashin ya caccaka wa mahaifiyarsa mai shekara 50 wuƙa a kanta da ƙirjinta da kuma sauran sassan jiki, inda ya tsere bayan aikata laifin.
Ga cikaken Video.