News

Allah Sarki: ku kalli bidiyon yadda ‘Yan bindiga suka mayar da mutanen Zamfara bayi bayan sace su a Masallacin Juma’a

Allah Sarki: Ku Kalli Yadda ‘Yan bindiga suka mayar da mutanen Zamfara bayi bayan sace su a Masallacin Juma’a

Rahotanni daga jihar Zamfara ta Najeriya na cewa, ‘yan bindiga sun mayar da mutane 44 da suka sace a Masallacin Jumu’a bayin dole, inda suke yi musu noma a gonarsu ta gero da dawa.

‘Yan bindigar sun kira ‘yan uwan mutanen ta wayar tarho, inda suka shaida musu cewa, yanzu haka suna nan suna yi musu noma, amma kawo yanzu ba su bukaci a biya su kudin fansa ba.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne ‘yan bindigar suka sace masu ibadar daga babban Masallacin Juma’ar garin Zugu da ke Karamar Hukumar Bukkuyum a jihar ta Zamfara.

Mazauna garin sun ce, ‘yan bindigar sun boye bindigoginsu a cikin tufafinsu kafin su yi wa masu ibadar dirar mikiya a daidai lokacin da babban limami ke gab da fara gabatar da huduba.

Jim kadan da shiga cikin Masallacin ne, ‘yan ta’addar suka fito da bindigoginsu tare da yin harbe-harbe.

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce, tuni ta fara farautar wadannan ‘yan bindigar domin ceto Masallatan daga hannunsu.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button