![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2021/08/FB_IMG_1628496691542.jpg?resize=720%2C405&ssl=1)
Babban Mai ‘Kera Boma-Bomai na Kungiyar Boko Haram, Musa Adamu Ya Mika Wuya.
Babban Mai Kerawa Kungiyar Boko Haram Boma Bomai Musa Adamu Wanda aka fi Sani da Mala Musa Abuja,
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2021/08/FB_IMG_1628496696168.jpg?resize=300%2C169&ssl=1)
Shida Mataimakinsa Usman Adamu wanda aka fi Sani da Abu Darda sun Mika wuya ga Jami’an Tsaro.
Sun dai mika wuyan ne tare da Iyalansu da Mabiyansu a Karamar Hukumar Bama, Jihar Borno
Mukaddashin Kwamandan (GOC) Sashi na 7 na Rundunar Sojin Najeriya, Birgediya Janar Abdulwahab Adelokun Eyitayo ne ya karbe su a hedkwatar 21 ta Special Armored Brigade dake Bama a ranar Asabar, 7 ga Agusta, shekarar 2021