News

BIDIYO: Allah Sarki Mahaifiyar Ummita Ku Kalli Bayanin Da Taiwa Manema Labarai Kan Yadda Dan China Ya Kashe Yarta A Gabanta

BIDIYO: Allah Sarki Mahaifiyar Ummita Ku Kalli Bayanin Da Taiwa Manema Labarin Kan Yadda Dan China Ya Kashe Yarta A Gabanta

Cikin Wata Tattaunawa Da Akai Da Mahaifiyar Ummita Wadda Ta Gamu Da Ajalinta Sakamakon Kisan Yankan Rago Da Wani Dan China Yai Mata.

Kamar Yadda Zaku Gani Acikin Bidiyon Dake Kasa, Mahaifiyar Ta Baiyana Cewa.

Dan Chinan Yazo Musu Har Gida Yanata Kwankwasawa, Sukuma Suka Ki Budewa.

Da Sukaji Abin Yayi Yawa Ne, Sai Mahaifiyar Ummita Taje Ta Bude Domin Taji Mai Yakawo Shi Yake Neman Balla Musu Kofa.

Bayan Ta Bude Ne Sai Ya Hankade Ta Ya Wuce Cikin Gidan Nasu Kai Tsaye, Tare Da Caccakawa Ummita Wuka.

Lamarin Da Yasa Ta Kwarma Ihu. Inda Yan Unguwa Suka Kawo Musu Dauki Tare Da Kama Dan Chainan.

Yanzu Haka Dai Shi Wannan Dan Chaina Yana Hannun Hukumar Yan Sanda Ta Jahar Kano.

Ita Kuma Ummita Ta Amshi Kiran Mahaliccinta Bayan An Garzaya Da Ita Asibitin UMC Dake Unguwar Jambulo A Kano.

Ga Bidiyon Ku Kalla

https://youtu.be/S3gNp2yrUuY

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button