News

BIDIYO: Yadda Dalibai Suka Fusata Suka  Qonata Da Ranta Har Lahira Kan Zagin Annabi

BIDIYO: Yadda Dalibai Suka Fusata Suka  Qonata Da Ranta Har Lahira Kan Zagin Annabi

Yadda lamarin ya faru

Wani ɗalibin kwalejin da BBC ta tuntuɓa ya bayyana cewa a lokacin da ɗaliban suka samu labarin faruwar lamarin, rigima sai ta kaure a cikin makarantar.

A cewarsa malamai da sauran shugabannin kwalejin sun yi ƙoƙarin su dakatar da ɗaliban daga wannan tarzoma amma abin ya ci tura, inda har jami’an tsaro suka je makarantar suna harba wa ɗaliban hayaƙi mai sa hawaye.

Ɗalibin ya bayyana cewa idan aka harba hayaƙin sai ɗaliban su ma su ɗauka su jefa wa jami’an tsaron. Ya ce ba ɗaliban kwalejin bane kaɗai suka tayar da hargitsin har da na waje suka shiga cikin kwalejin.

A cewarsa, wadda ake zargi da aikata saɓon an ɓoye ta a ɗakin jam’ian tsaro da ke ƙofar kwalejin inda masu tarzomar suka sha ƙarfin jami’an tsaron suka ɓalla ƙofar ɗakin suka ciro yarinyar.

Ya ce an yi ƙone-ƙone da farfasa muhimman kayayyaki a cikin kwalejin musamman motocin malamai.

Me jami’an tsaro suka ce
Rundunar ƴan sandan Najeriya reshen Jihar Sokoto ta tabbatar da faruwar wannan tarzoma sai dai ba ta yi ƙarin bayani kan abubuwan da suka faru ba inda suka ce suna gudanar da bincike.

ASP Sanusi Abubakar wanda shi ne mai magana da yawun ƴan sandan ya ce ƴan sandan tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro sun bazama a yankin kuma a yanzu akwai kwanciyar hankali.

Ya ce ba su da tabbaci kan maganganun da ake yi na cewa wasu sun rasa ransu haka kuma bai tabbatar da ko an kama wani daga cikin masu tarzomar ba.

Bugu-da-kari ASP Sanusi yace idan akwai wani karin bayani musamman daga binciken da suke yi za su sanar nan gaba.

Tuni dai hukumomin kwalejin ilimi ta Shehu Shagari da ke Sokoto suka sanar da rufe makarnatar har sai abin da hali yayi.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button