Kannywood News

BIDIYO: Yanzu Yanzu Baban Chinedu Ya Tona Asiri Kan Rikicin Naziru Sarkin Waka Da Nafisat Abdullahi

BIDIYO: Yanzu Yanzu Baban Chinedu Ya Tona Asiri Kan Rikicin Naziru Sarkin Waka Da Nafisat Abdullahi

Tun Da Nafisah Abdullahi Ta Fice A Fim Din Labarina, Naziru Ya Zauce, Sai Maganganu Marasa Kai Yake Yi, Cewar Jarumi Kuma Mawaƙi, Baban Chinedu

Fitaccen ɗan wasan finafinai Hausa kuma shahararren mawaƙi Baban Chinedu kwance wa Naziru Ahmed Sarkin Waka zani a kasuwa in da ya fallasa ainihin abinda ya sa Nafeesat ta fice daga fim din labarina.

A cikin wani bidiyo da ya saka a shafin sa ta facebook, Baban chinedu ya ce, gaba daya Naziru ya dimauce ya shiga ruɗu sabida Nafeesat.

Da zarar Nafeesat ta ce gashi, sai ya kasa barci yayi ta ɓaramɓarama, yana kame kam, yana zazzaro ido da jijiyoyin wuya.

” Kawai don Nafeesat ta fice daga fim ɗin Labarina shikenan ya ruɗe. Duk abinda ta ce sai ya ce sai maida mata da martani. Kana cutan mutane baka so ayi maka magana. Kai waye. Ina ruwan mu da wani sarkin wakar ka. Akwai sarkin kasuwa ma, akwai sarkin ƴan daudu.

” Kana saka talla a fim wanda ake biyan ka maƙudan kuɗaɗe amma kuma kana ba masu fitowa a fim ɗin dubbai kai mkuma kana shake miliyoyi. Ba dole su fice daga fim ɗin ba.

” Ga shi yanzu ai dole ka daina fim din da karfin tsiya. Kai mawaƙi ne. Ba huruminka bane yin fim. Saboda haka dole ka dakatar da fim ɗin, babu yadda ka iya.

” Kai dai baka oya fim ba, in ka isa kuma ka fito kayi fim din ka ga ko za a kalla.

Idan ba a manta ba, Nafeesat ta rubuta a shafinta cewa iyaye su daina haifan ƴaƴan da ba zasu iya kula da su ba.

Awowi bayan ta faɗi haka sai Naziru ya maida mata da martani cewa ƴaƴan.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button