
DA DUMI-DUMI: Mutane da dama ne suka mutu sakamakon fashewar bam a wani cocin Ondo a ranar Lahadi, yayin da Kiristoci Suke gudanar da ibada.
Mazauna garin sun shiga cikin fargaba bayan da wani bam ya tashi a cocin St Francis Catholic da ke titin Owa-luwa a karamar hukumar Owo ta jihar ranar Lahadi.

Kamar yadda jaridar PUNCH ta ruwaito, wasu masu gudanar da ibada sun rasa rayukansu sakamakon lamarin.
Fashewar, rahotanni sun ce ta afku ne a harabar cocin a lokacin da jama’a ke ci gaba da gudanar da taron.
Lamarin ya haifar da barkewar Fargaba sosai a yankin yayin da mazauna unguwar da ke yankim suka gudu domin tsira da rayukansu.
Har ila yau an ce an dakatar da harkokin kasuwanci da zamantakewa a garin.
Wata majiya kuma ta ce wasu makiyaya ne da ake zargin sun kai hari coci tare da kashe masu ibada.
A cikin wani faifan bidiyo da aka yi a shafin yanar gizo na Twitter, an ga gawarwakin masu bautar da ba su da rai a kwance a cikin jini.
Gory ðŸ˜ðŸ˜.. Now, they want to establish their kingdom of bloodshed in Southwest and Ondo State is their first target.
The bomb explosion at St. Francis Catholic Church, Owo must not give them the assurance that they can extend their terror to other parts of the country. pic.twitter.com/JEGCOTsnK2— President Eniola Daniel (@UnlimitedEniola) June 5, 2022