News

DA DUMI-DUMINSA: Gwamntin Jahar Borno Ta Hana Gudanar Da Zanga-zanga Kan Kalaman Batanci Da Wata Budurwa Ta Sake Yi

DA DUMI-DUMINSA: Gwamnatin Jihar Borno Ta Hana Musulman Jihar Gudanar Da Zanga-zangar Nuna Bacin Ransu Kan Munanan Kalaman Batanci Da Wata Budurwa Ta Yi Akan Fiyayyen Halitta Annabi Muhammad SAW A Jihar.

A safiyar yau Litinin daruruwan mutane sun yi dafifi kan titin Division 7 dake Maiduguri domin yin zanga-zangar nuna bakin ciki kan kala*man ba*tanci ga Annabi Muhammad SAW da wata mai suna “Noami Goni” ta wallafa a shafin sada zumunta na Facebook wanda ya haifar da ri*kici a yankin.

Gwamnatin jihar ta tura jami’an rundunar da suka hada da sojojin Najeriya, ‘yan sandan Mobile, jami’ai masu yaƙi da ta’addanci ‘Counter-Terrorism Unit’ (CTU), Anti-Bomb Squad (EOD), “Crack Team” NSCDC, a yankin domin kwantar da tarzoma da halin da ake ciki.

Har zuwa yanzu da muke kawo muku wannan rahoton, ba a ka*ma budurwar ba.

Me za ku ce?

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button