![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/11/Screenshot_20221010-151831_1.jpg?resize=703%2C372&ssl=1)
Innalillahi wainna ilaihirrajiun Dalibar Ajin Karshe a Jami’ar Usman Danfodio ta rasu tare da ‘Yar ta a Hatsarin Mota.
Innalillahi wainna ilaihirrajiun Dalibar Ajin Karshe a Jami’ar Usman Danfodio ta rasu tare da ‘Yar ta a Hatsarin Mota.
Innalillhi wa inna ilaihi raji’un: Yanzu muka sami wani labari daga shafin Hausaloaded kamar yadda suma suka samo labarin daga shafin Dailynigerian, inda suka wallafa labarin wata mata mai suna Sha’awanatu.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/11/FB_IMG_1668070345461.jpg?resize=144%2C300&ssl=1)
Ga dai yadda suka wallafa labarin kamar haka.
Sha’awanatu na tafiya hutun sabuwar shekara tare da mijinta a lokacin da ta samu hatsarin mota a ranar 23 ga Disamba, 2021 a kan hanyar Talata Marafa- Gusau, kan hanyar zuwa gidanta da ke Zariya daga jami’arta da ke Sakkwato.
Hadarin ya yi sanadiyar mutuwar diyarta Khadijah mai shekaru uku da haihuwa kuma Sha’awanatu ta samu rauni a ciki da kuma ta jiki.
Sha’awanatu Imran ta rasu ne a daren ranar Asabar da ta gabata da misalin karfe 9:17 na dare bayan ta shafe kwanaki 36 tana jinya a asibitin Shika Zaria.
Muna mata Addu’a Allah yaji kanta da rahama ameen.