![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2021/04/Capture-2021-04-16-16.04.59.jpg?resize=780%2C470&ssl=1)
Rahotanni Daga Jamhuriyar Niger Na Cewa An Gudanar Da Jana’izar Yara Yan Makarantar Boko Su 20 Wadanda Iftila’in Gobara Yai Sanadiyar Rasa Rayukan Su
A ranar 14 ga watan nan da muke ciki ne gobarar ta tashi a wata makarantar boko dake anguwar pays bass a babban birnin yamai.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2021/04/FB_IMG_1618598363692.jpg?resize=225%2C300&ssl=1)
Haka zalika rahoton ya kara da cewa kimanin ajujuwa 25 acikin 35 iftila’in gobarar ya shafa wanda kuma yai sanadiyar rasa rayukan yara kananu masu shekaru 5 zuwa 10.
Kazalika wannan iftila’in gobara ya daga hankulan mutane da dama musamman ma a jamhuriyar ta niger dakuma kasar nigeria
Anan muke addu’ar ubangiji Allah Ya Jikansu Yakuma bawa iyayensu hakurin jure wannan rashi ubangiji ya kiyaye gaba Amin.