News

Kai Tsaye Daga Gurin Jana’izar Yan Makarantar Da Gobara Ta Hallaka A Jamhuriyar Niger

Rahotanni Daga Jamhuriyar Niger Na Cewa An Gudanar Da Jana’izar Yara Yan Makarantar Boko Su 20 Wadanda Iftila’in Gobara Yai Sanadiyar Rasa Rayukan Su

A ranar 14 ga watan nan da muke ciki ne gobarar ta tashi a wata makarantar boko dake anguwar pays bass a babban birnin yamai.

Haka zalika rahoton ya kara da cewa kimanin ajujuwa 25 acikin 35 iftila’in gobarar ya shafa wanda kuma yai sanadiyar rasa rayukan yara kananu masu shekaru 5 zuwa 10.

Kazalika wannan iftila’in gobara ya daga hankulan mutane da dama musamman ma a jamhuriyar ta niger dakuma kasar nigeria

Anan muke addu’ar ubangiji Allah Ya Jikansu Yakuma bawa iyayensu hakurin jure wannan rashi ubangiji ya kiyaye gaba Amin.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button