News

Yadda Wasu Matasan Musulmai Suka Yi Dawainiyar Jinyar Abokinsu Kirista Har Zuwa Lokacin Jana’izarsa Bayan Ya Mutu A Jos

Yadda Wasu Matasan Musulmai Suka Yi Dawainiyar Jinyar Abokinsu Kirista Har Zuwa Lokacin Jana’izarsa Bayan Ya Mutu A Jos

Wasu Matasa Musulmai A Jahar Plateau Sunyi Dawainiyar Jinyar Abokin Su Kirista Mai Suna Issac Har Sai Da Rai Yai Halinsa.

Wannan matashi mai suna Isaac Adamu ya mutu a ranar 5 ga watan Yuli bayan fama da rashin lafiya. Mazaunin unguwar Dadin-Kowa ne dake garin Jos jihar Filato.

Tuni aka yi jana’izarsa a makabartar COCIN dake Kangang.

Saidai wani darasin dauka a mutuwar Isaac shine lokacin da yake kan jinya, abokansa wadanda yawanci musulmai ne sun kasance tare da shi a koda yaushe.

Sun dinga bada gudummawar kudin jinyarsa a asibiti, haka ma bayan mutuwar sa abokan nasa musulmai sun tallafawa mahaifinsa har aka kammala jana’izarsa.

Masu karatu wane darasi kuka dauka a wannan labarin?

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button