![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/05/Capture-2022-05-03-09.46.47.jpg?resize=780%2C470&ssl=1)
Ƙasar Saudiya Ta Cafke Ƴan Najeriya 20 Masu Ɗaga Hotunan Ƴan Siyasa A Ɗakin Ka’abah
Hukumomi a ƙasar Saudiyya, sun cafke mutane 20, da aka kama su na daga Hotunan Bola Tinubu da sauran wasu Ƴan siyasan Najeriya a gaban ɗakin Ka’aba, a cewar hukumomin za a hukuntasu.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/05/FB_IMG_1651567461401.jpg?resize=232%2C300&ssl=1)
Majiyar ta cigaba da cewa a yanzu haka suna hannun mahukunta ƙasar, ƙarƙashin kulawar askarawa domin gurfanar dasu gaban kotu tare da yanke masu hukunci dai-dai da abinda suka aikata, majiyar kuma ta cigaba da cewa babu shakka zasu kwashi kwashin su a hannu.
Majiyar mu ta kuma jiyo cewa, hukumomin sunce Sam baza su laminci ire-iren waɗannan abubuwan da ‘Ƴan Najeriya suke ba, domin yin wani abu na daban a cikin ƙasar su ba, domin kuwa wannan sabon wani abu ne dasu ba Susan da shi ba.”
DAGA Shafin Arewa Media