![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/03/Capture-2022-03-04-20.46.53.jpg?resize=780%2C470&ssl=1)
Hanifa: Kotu ta wanke matar Abdulmalik Tanko
Kotun Majistire mai mai lamba 12 da ke zaman ta a gidan Murtala, Jihar Kano, ta wanke Jamila Sani, matar Abdulmalik Tanko, wanda a ke zargi da garkuwa da kuma kashe Hanifa Abubakar.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/03/FB_IMG_1646423054002.jpg?resize=300%2C219&ssl=1)
A jiya ne dai Babbar Kotun Jiha mai lamba 5, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Usman Na-abba, ta gayyaci Jamila domin ta bada shaida a kan Tanko, bayan da ya musanta cewa shi ya kashe Hanifa.
A yau ne a ka gurfanar da Jamila a Kotun Majistare ɗin, bayan da Tanko ya ce a gidansa ya ajiye ta, a hannun matarsa.
Da ya ke yanke hukunci a kan tuhumar da a ke mata, alƙalin kotun, Muhammad Jibril ya wanke Jamila bisa hujjar cewa babu hannun ta a ciki.
Alƙalin ya ce hasali ma, ƙarya Tanko ya yi wa matar tasa da cewa Hanifa ƴar gidan wata malama ce mai aiki a makarantar sa da ta samu aiki a Saudiyya, shine ta je Abuja domin kammala shirin tafiya Saudiyan.
Da ga ƙarshe alƙalin ya wanke ta ya kuma bada umarnin a sake ta sabo da ba a same ta da hannu a cikin laifin ba.
https://youtu.be/lUwm0j7w1NE