![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/09/FB_IMG_1663879884290.jpg?resize=720%2C405&ssl=1)
BIDIYO: Yadda Ambaliyar Ruwa Ke Kwashe Motoci Tare Da Rushe Gidaje A Birnin Lagos
Wani Rahoto Da Muke Samu Yanzu-Yanzu Na Cewa, Ambaliyar ruwa na neman shafe birnin Legas da ke Najeriya.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/09/nnimages-62.jpeg?resize=300%2C169&ssl=1)
Yayin da mazauna Legas da ke Najeriya, ke ci gaba da fuskantar matsalar ambaliyar ruwa kowacce shekara.
musamman a watannin Maris zuwa Nuwamba, a ‘yan shekarun nan yankin na fama da mummunan matsalar ambaliyar ruwa.
Wannan na zuwa ne dai-dai lokacin da hukumomi a Najeriya ke ci gaba da gargadin aukuwar wata ambaliyar nan da dan lokaci kadan.
Haka zalika masana na ganin cewa birnin na Legas ya fara nutsewa a cikin ruwa, sakamakon matsalar dumamar yanayi.
Latsa Bidiyon Nan domin Kallon rahoton Shamsiyya Haruna.
https://youtu.be/b2its-OvOh4