![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/05/FB_IMG_1652535372003.jpg?resize=720%2C405&ssl=1)
BIDIYO: Yanzu-Yanzu Gwamnati Ta Saka Dokar Hana Fita A Jahar Sokoto Ta Tsawon Awa 24
Gwamnatin Jihar Sokoto ta saka dokar hana fita ta tsawon awa 24 a jihar sakamakon zanga-zangar da wasu mazauna jihar suka gudanar a yau Asabar.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/05/FB_IMG_1652521901506.jpg?resize=300%2C225&ssl=1)
Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce dokar za ta fara aiki nan take.
An ɗauki matakin ne “saboda dawo da doka da oda a birnin Sokoto da jihar baki ɗaya”, a cewar sanarwar.
Masu zanga-zangar na nemanjami’an tsaro su saki mutanen da suka kama da ake zargi da kisan matashiyarda ke karatu a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari, wadda suka zarga da zagin Annabi Muhammadu (SWA).
Ku Kalli Bidiyon Anan