News

Innalillahi Wa Inna Ilaihir Raju’un Wani Dan Majalisar Dokokin Jihar Katsina Ya Rasu Yayin Da Ya Ke Aikin Umrah

Innalillahi Wa Inna Ilaihir Raju’un Wani Dan Majalisar Dokokin Jihar Katsina Ya Rasu Yayin Da Ya Ke Aikin Umrah

Wani Dan Majalisar Dokokin Jihar Katsina Ya Rasu Yayin Da Ya Ke Aikin Umrah

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Bakori a majalisar dokokin jihar Katsina Dr. Ibrahim Aminu Kurami ya rasu a kasar Saudiyya da misalin karfe biyu na safe agogon Najeriya, yau Litinin yayin da yake aikin Umrah kuma an yi jana’izarsa a Madina.

Shugaban kwamitin yada labarai na majalisar, Ali Al-Baba, ya tabbatar da faruwar lamarin. Ko da shike Al-Baba mai wakiltar mazabar Katsina a majalisar bai bayar da cikakken bayani game da rasuwar Kurami ba, ya ce shi da sauran ‘yan majalisar za su kai ziyarar ta’aziyya a garin Kurami da kuma mazabar Bakori na marigayi dan majalisar bayan taron bitar da suke yi a garin Kano.

Kurami dan majalisar wakilai ne na jam’iyyar All Progressives Congress wanda kuma ya lashe zaben fidda gwani na karshe na wakiltar mazabar karkashin jam’iyyar a zaben 2023 mai zuwa.

An zabi Kurami ne a matsayin dan majalisar dokokin jihar Katsina mai wakilai 34 a zaben cike gurbi na ranar 31 ga watan Oktoba, 2020, bayan rasuwar magabacinsa Abdurrazak Ismail Tsiga.

Marigayin ya bar mata biyu, ‘ya’ya 11, da jikoki uku.

https://youtu.be/Ac8nwJYmosM

 

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button