News

Ku Yafe Mu Karku Bari Yunwa Ta Kashe Mu, Yan Kudu Sun Roki Hausawan Arewa


Tun biyo bayan rikicin kabilanci a kudancin nigeria wanda yai sanadiyar mutuwar hausawa fiye da dari tare da asarar dimbin dukiyar hausawa fataken abinci.

Shugabannin kungiyar hausawa masu safarar abinci izuwa kudu suka umarci mambobin su da su dakata da kai kayan abinci kudancin nigeria har sai gwamnati ta dauki mataki akan kisan gilla da cin kashin da ake musu tare sa biyan fansar asarar da sukai.

Lamarin da yakai ga assasa hauhawar farashin kayan masarufi a yankin kudancin nigeria .

Kasuwar Mayanka Inda Ake Saida Naman Shanun Da Yan Arewa Suka Kai Kudu.

Wanda kuma kullum abin qara sama yakeyi tare da barazanar qara jefa yankin na kudu cin qangin talauci.

A wani rahoto da jaridar madubi- H suka fitar a shafin su na Facebook Sun bayyana cewa.

Alummar yankin kudu na rokon yan arewa fataken abinci da suwa Allah Su Yafe Musu tare da janye wannan yajin aikin.

Su cigaba da kawo musu kayan abincin Inda Suka Alwashin hakan bazai sake faruwa ba.

Kasuwar Kayan Miya Inda Ake Saida Kayan Miyan Da Yan Arewa Suka Kai Kudu.

Sai dai mutane da dama na bayyana ra’ayoyin su akai yayinda suka ke cewa ko za’ai musu afuwar to a bari su ji a jikinsu tukunna.

A gefe guda kuma waau ke ganin tunda sun gane kuren su harma sun fto da kansu sun nemi yafiya to a yafe musu kawai zaifi.

Anan mukeso da ku bayyana mana ra’ayoyinku. Shin yakamata a janye wannan yajin aikin haka? Ko kuma aci gaba har sai gwamnati ta dauki matakan da suka dace tare da biyan yan arewa diyyan asarar da sukayi?

Related Articles

32 Comments

  1. Wlh baikamata ayafebamusu ba harsai gwannati tabiya diyya, idan kuma taqi biya acigaba da yajin aiki harsai tabiya diyar.

  2. A gaskiya bama goyon bayan yin yafiya ga al,Umar kudancin kasarnan hard Sai gwamnati ta biya diyar asarar rayuka da dukiyoyin mutan arewa sannan da daukar doka Mai tsanani ga duk wanda yai kokarin tada wata fitina makamancin wannan Allah ka zaunar damu lafiya

  3. Agaskiya suhu tsakaninmu dasu bayayi harsai gwamnati tashigo ciki taduba lamarin kuma da yarjejeniyar wani abu makamanci haka bazai sake faruwaba

  4. Ra ayina shine acigabada yajin aikin da akeyi na dakatar da kai abinci kudan cin Nigeria harsai manyansu sunyi maganar da yakamata sunbada hakuri tareda neman sulhu.

  5. maganar dasukecewa suntuba kawai sun fada abakine amma bataikai har zuci ba idan kuma aka kuskura akabiyema dadin bakinsu to za’akoma yar gidan jiya saboda su yan kudu da zasu samu dama to sai sunfidda mu daga nigeria idan kuma akayafe masu to sai sunci amanarmu saboda basuda rukon amana

  6. Kada ayi gaggawar yi masu afuwa, domin kuwa mai hali baya barin halinsa. Wai harma daga cikin manyansu sun fara cewa suma zasu rike man fetur? kamar arzikin Nigeriyar nasu ne suka dai. Dan Allah mudaina wannan shawarar tukuna. Ya kamata mu kasance masu kishin kanmu. Kuma muna kara jaddada godiyarmu ga manyanmu wadanda suka nuna kishi akanmu, Allah ya cika maku burinku na alheri ya kuma saka maku da mafificin alkairinsa. Kuma mun San wayanda sukayi gum da bakunansu domin kwadayin duniya. Allah ya tabbatarda ni’imarsa da kwanciyar hankali a Arewarmu dama Nigeriya baki daya.

  7. Sadeeq Daga kano bama goyon baya ajanye har sai gwamnati ta shiga lamarin an biyamu diyyar rayukan “yan uwanmu Hausawa da aka kashe sannan muga yiwuwar sulhu, mu bazamu kashe su da makami ba.

  8. Aa koyarwarmu(musulunci)cewa yayi : mafifici acikinku shene wanda alumma sukafi amfana! Bawai Dan wani yankiba,sabo da haka ko ancigaba da kai musu mune muke da rinjaye da izinin Allah,

  9. Ya Kamata a samu kyakkyawar matsaya a tsakani kafun a janye wannan yajin aiki, kuma koda za’a janye a Bari sai sunji har zuciyarsu kuma su tabbatar da irin Alkhairi da Yan arewa suke dashi a Nigeria baki daya… Allah ya bamu damuna Mai Albarkah kuma ya tabbatar mana da zaman lafiya a kasar mu Nigeria baki daya… Amiin

  10. A bari su kara ji ajikinsu su da Kansu zasu fadawa gwamnati tayi intervening tunda anfijin maganarsu fiye da ta Dan arewa

  11. Agaskiya ni anawa ra,ayi kar ayi gaggawar yafemasu sai sungane munada rana agaresu yinhakan shizaisa musamu kwanciyar hankali agaresu sannan yakamata asa subiya diyyar asarat rayukan da sunkawa yan rewa domin yan arewa surage radadi ina fatan gomnati zataduba tayimuna adalci Allah yasa haka ameen.

  12. Gsky baikamata ayafe musu bah a wnn lkcn, har sai gwamnatin Nigeria ko ta jahohin sun biya haddin adadin jamaar daaka kashe da kuma biyan asarar makudan dokiyoyinsu dasukayi

  13. Baikamata ayi saurin yafe masu ba kashe rai bawasa bane sun dauki rayikan yan arewa ba bakin komaiba abrsu sukaraji ajikinsu

  14. Ni ina goyon bayan a cigaba da yajin aiki, domin mu Hausawa ba bayin yankudu bane, kuma muna ragamusune saboda Addinin Musulunci baya san tashin hankali da rigima shiyasa duk abinda sukei mana muke yin hakuri, kuma Addinin Muslunci ya yarda da idan akayimaka laifi to kanuna anyimaka laifi, toh don haka wannan yaji aikn nuni ne akan a batamana rai, mu Hausawa muana da hankali kuma muna san zaman lafiya amma bawanda zamu kashe ko daka ko mu konawa dukiya domin musulunci ya hana zalunci, ammafa kisani shiru shiru ba tsoro bane, don haka saiku kiye gaba.
    Kuma yanzu kun fahimci zamu iya rayuwa ba man fetur, don ba dole bane kuma ba a cinsa kuma ba a shansa, don haka kuma sai kurayu da abunku, kubarmaba kayan abincinmu muma murayu dasu.
    Kuma yajin aikin kai kayan abinci kudu yanzu muka Fara bagudu baja dabaya. Allah ka taimaki Arewacin Nigeria.

  15. Aci gaba har sai gwamnati ta dauki matakan da suka dace tare da biyan yan arewa diyyan asarar da sukayi.
    Bayan hakama kar akaimusu komai nakayan abinci, tinda sunagadara da fetur, susha fetur nasu, kowa yarike nasa nan da shekara daya 1 tak, aga waye zaiji jiki.

  16. Tukuna dai, ai idan aka kyalesu kaman rayukan yan’uwanmu sun tafi a banza kenan. Suma a barsu jikinsu ya Gaya musu tukuna, se sugane amfaninmu.

  17. Mu Yan arewa bama buqatarsu ko anyi sulhu baida amfani Dominic dukyadda Kai da jaki said yachi kara

  18. To ai dama idan kaga Allah ya hada alumma to hakan shine dai dai da zaman alummar mu duka bamuda kasar tinkaho bayan nigeria saboda haka ya kamata mu girmama junanmu ba tashin hankali ba amma wannan mataki shine dai dai kuma hakan ya kamata idan munada amfani garesu zasu gane kuma ina goyon bayan a cigaba da hakan har sai gwamnati ta dauki matakin da ya kamata idan mutanen kudu suka zo gurinmu mu a girmamasu bama cutar dasu amma su sai su cutar damu kuma a sanya ido bana goyon baya ni idan son samu na ne a bari har sai yunwar da suke fada ta fara kashe su sannan matsiyata marassa sanin ya kamata

  19. Agaskiya mutanan gudu walkancin da sukemana yakai makura Ni anawa ra’yi subiya diyya narayuka da dukiyoyi dacin mutunci

  20. Gaskiya
    Yakamata
    Ko za”ayafe musu
    Abarsu suji sosai ajikinsu
    Ko za Su gane cewa mu mutanine masu
    Matukar amfani a Nigeria…
    Dan haka a kyalesu zuwa rabin shekara..

  21. Wallahi mutanen kudancin Nigeria basuda adalci ko kadan, da zarar wata yar hatsaniya ta tashi gurinsu shine su kone motoci da kayayyakin yan arewa, dama kashe mutanen mu na arewa masu zama can, kawai abari su jiya ajikinsu ayita yajin aikin koda na wata guda ne, sai kowa yasan matsayinshi.

  22. Mudai kullum addu’armu shine samun zaman lafiya sa’annan damuma zamu dauki makami toda abinbazaiyi kyau ba saboda haka muna kara hama jama’ar kasarmu Nigeria mazauna yankin kudanci kunne dasuyiwa Allah su zauna lafiya domin sunkusa kaemu bango

  23. Ai ina rakon shuwagaba n arewa acikgaba da yajin Ai kin nan muga zuwa shekara daya ko six month ko sun gane mahiman cin yan arewa

  24. Gaskiya hai kamata ataye musu ba nikirana shine kwana kwana aqauracewa Kai musu abinci tunda Ana iya kaiwa qasashe maqotanmu kamar nijar ghana dasauransu arabu da yankudu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button