News

Tabbas Rayuwar Yarabawa Na Cikin Wani Hali. Kan Hau Hawar Farashin Kayan Abinci Wanda Basu Taba Gani Ba


Yadda Kayayyakin Abinci Ke qara Tsada A Kudancin Nigeria Sakamakon Kin Shigar Da Kayan Da Yan Arewa Suka Daina.

Lamarin dai ya faru ne biyo bayan wani rikici da ya barke a wata kasuwa dake jahar oyo wanda yai sanadiyar salwantar rayuwaka dakuma dimbin dukiya.
Rikicin dai yafi shafar hausawan kasuwar dakuma wasu dake zaune a cikin jahar oyo.
Hausawa na zargin manyan yarabawa da iza wutar rikicin tare da nuna halin ko in kula da cin kashin da ake musu.
Dankalin Da Ake Kaiwa Kudu Daga Yankin Arewa
Shugabannin yan kasuwa Daga Arewa sun fusata gami da shiga yajin aikin dena kai kayan abinci kudu har sai an biya diiyan wadanda aka kashe tare da biyan su kudaden da sukayi asara.
Rahotanni na bayyana cewa kwana biyu da fara wannan yajin aikin dena kai kayan abinci kudu.
Kasuwar Tumatur Da Hausawa Ke Kaiwa Kudu Daga Arewa
Hakan tasa yan kudun ke kokawa tare da fuskantar siyan kayan abinci da tsadar gaske a garin.
Ku bayyana mana ra’ayoyinku Kuna goyan bayan wannan yajin aikin? Ko kuma hakan bai dace ba?

Related Articles

21 Comments

  1. Tabbasa yanxu ne hausawa suka fara sanin ciwan kansu kam kuma sunyi daidai wlh nifa fa da sansamu nema fa araba kasarnan wlh kowa yasan gidan ubansa aiπŸ™„πŸ™„πŸ™„πŸ™„

  2. Ai abinda yan kasuwa sukayi yayi dai dai ba sunce su sunfi kowa arziki ba Kuma sun raina mu suna ganin mu bama tafuka komi suke da komi to ai yanzu sai su sha man fetur dinsu

  3. Ih Muna goyon bayan hakan Sai dai:
    Ina da Kira na musamman ga masu ruwa da tsaki arewacin kasarnan, da su yi kokarin inganta harkokin noma kiwo kasuwanci harkar tsaro, saboda ashirye muke mu dawo muci gaba da zama yankunan mu, Daman can tsadar rayuwa ce takai mu ga yin balaguro zuwa kudancin kasar, har muka tsinci kanmu cikin yanayin wulakantawa, ana Mana kallon bakin haure, wannan shine shawarana ga wadanda abin yashafa, amma in ba hakaba to za’a gudune Kuma baza’a tsiraba

  4. Hakan yayi daidai amma yanada kyau Buhari ya kwatomana hakkinmu kuma y biya wadanda aka kashe yanuwansu diyya DA wadanda akayima asara sannan a zauna adaidaita lamarin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button