News

Masha Allah: Matar data Cakawa Yarin Wuka Tashiga Hannu A Kano

Cikin wata sanarwa da kakakin ƴan sandan jihar Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce matar mai suna Fatima ta ɗauki yarinyar ce zuwa wani gida da ba a kammala ginawa ba, inda ta daba mata wuƙa a wuya da ciki sannan ta gudu ta bar ta a wurin.

Yan sanda a Kano sun ce sun kama wata mata mai shekara 35 da ake zargi da daba wa wata yarinya wuƙa a karamar hukumar Kumbotso na jihar.

Kiyawa ya ce an kuma kama mijin matar, inda ya yi iƙirarin cewa tana da matsalar kwakwalwa tare da cewa bai san wajen da take ba, inda daga bisani kuma aka cafke ta a ranar Alhamis a maɓoyarta a kauyen Dungulmi a karamar hukumar Dutse na jihar Jigawa.

Ya zuwa yanzu dai ƴan sanda na ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin da ya faru a ranar Lahadi 14 ga watan Afrilun, 2023.

Matar da ake zargi dai ta amsa aikata laifin da ake tuhumarta da shi, inda ta ƙara da cewa ta daba wa yarinyar wuƙa ne don ramuwa, saboda a cewarta mahaifin yarinyar yana bai wa mijinta shawarar cewa ya ƙara aure.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button