Politics

Tirqashi: EFCC ta kammala shirin kama wasu gwamnonin Najeriya

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Najeriya, wato EFCC ta kaddamar da gagarumin bincike akan wasu gwamnonin kasar da mataimakansu dake shirin mika mulki a ranar litinin mai zuwa, sakamakon kawo karshen kariyar tuhumar da suke da ita kamar yadda doka ta tanada.

Ofishin hukumar EFCC da ke Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya.

Wani bincike da Jaridar Premium Times da ake wallafawa a Najeriya ta gudanar, yace Hukumar EFCC ta baza komarta domin cafke wasu daga cikin gwamnonin da mataimakansu 28 dake shirin sallama da gidajen gwamnati a makon gobe.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Najeriya, wato EFCC ta kaddamar da gagarumin bincike akan wasu gwamnonin kasar da mataimakansu dake shirin mika mulki a ranar litinin mai zuwa, sakamakon kawo karshen kariyar tuhumar da suke da ita kamar yadda doka ta tanada.

Jaridar tace hukumar tayi shiri tsaf domin ganin wadannan gwamnoni basu gudu sun bar kasar ba, bayan mika mulki ga wadanda zasu gaje su a ranar litinin mai zuwa.

Binciken yace tuni EFCC ta bukaci takardun kadarorin da wadannan gwamnoni suka cika kafin fara aiki, wanda ya bayyana irin dukiyar da suka mallaka a wancan lokaci, yayin da kuma take dakon wadanda zasu bayar ayanzu domin nazari akansu.

Ko a makon jiya, shugaban hukumar Abdurasheed Bawa, ya dada jaddada shirin EFCC na bin diddigin wadannan gwamnoni da mataimakansu dake shirin sauka, sakamakon korafe korafe da kuma zarge zargen da ake musu da rub da ciki da kudaden talakawa.

Daga cikin gwamnonin da Bawa ya bayyana, akwai na Jihar Zamfara, Bello Matawalle wanda yace ana zargin sa da karkata akalar naira biliyan 70 mallakar jihar, yayin da gwamnan yace yarfe shugaban EFCC ke masa, saboda yaki bashi cin hancin naira biliyan 2 da ya nema a wurinsa.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button