News

Yadda Akai Bikin Bude Wani Titi A Jami’ar Maryam Abacha Wanda Aka Sadaukar Da Sunan Titin Ga Marigayiya Haneefa Abubakar

Jami’ar Maryam Abacha ta karrama Marigayiya Haneefa…

Biyo bayan zargin garkuwa da kisan yarinya Haneefa da wani malaminta na makarantar boko mai suna, Abdulmalik Muhammad Tanko, yayi.

A baya bayan nan, a yankin Kwanar Dakata dake karamar hukumar Nasarawa a jihar Kano.

Reshen jami’ar Maryam Abacha dake Nigeria, ta karrama Marigayiya Haneefa ta hanyar sanya sunanta a guda cikin titinan makarantar.

Yayin tattaunawarsa da manema labarai, shugaban jami’ar Farfesa Adamu Gwarzo, ya bayyana rasuwar Haneefa a matsayin mutuwa mai taba zuciya.

Wanda kuma hakan ne yasa suka ga dacewar su sanya sunanta a makarantarsu, domin tunawa da ita.

Mahaifin Haneefa, Abubakar Abdussalam, shi ne ya yanka kyallen bude allon da aka rubuta sunan Haneefa a guda cikin titinan jami’ar, ya bayyana godiyarsa bisa wannan karamci da sadaukarwa da aka nuna masa.

📷 Facebook/President MAAUN

Nasara Radio 98.5 FM
31/1/2022

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button