ReligionNews

Yanzu-Yanzu: Hukumar Hisba ta kama wasu Matasa dake cin Abinci da Tsakar Rana

A Yau talata ne hukumar hisbah ta jahar kano ta kama wasu matasa dake cin abinci da rana tsaka ana azumin ramadan.

Yan hisban sunyi nasarar kama matasan ne a karamar hukumar dawakin kudu Dake jahar kano.

Kamar yadda nasara radio suka wallafa a shafinsu na facebook cewa hukumar hisbah ta kama matasan ne da rana tsaka suna cin abinci.

Wannan lamari ya daurewa mutane kai kasancewar an kama matasan ne a jahar kano.

Anan mukeso da ku bayyana mana ra’ayinku dangane da wannan balahirar matasan da aka kama suna cin abinci da rana tsaka

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button