![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/02/FB_IMG_1645633490210.jpg?resize=720%2C324&ssl=1)
YANZU-YANZU: Majalisar Zamfara ta tsige Mataimakin Gwamnan jihar, Mahdi
Majalisar Dokoki ta Jihar Zamfara ta tsige Mataimakin Gwamna, Mahdi Aliyu Gusau.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/02/FB_IMG_1645633473026.jpg?resize=300%2C286&ssl=1)
A zaman majalisar na yau Laraba, ƴan majalisa 20 cikin 21 ne su ka zaɓi a tsige Mataimakin Gwamnan bayan da a ka miƙa ƙudurin cire shi ɗin.
Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa a jiya Talata ne dai kwamitin bincike da a ka kafa domin tuhumar Mahdi ɗin ya zauna jiya, amma kuma Mataimakin Gwamnan bai halarci zaman ba.
Sai dai kuma bayan da kwamitin ya miƙa rahoton da gaban majalisar a yau, sai mambobin su ka zaɓi su tsige Mataimakin Gwamnan.
Ƙarin bayani na nan tafe…