![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2021/04/FB_IMG_1619006197754.jpg?resize=720%2C470&ssl=1)
Rahotanni Daga Jaridar TVC na cewa, Majalisar Wakilan Nigeria Tayi Watsi da wani kudiri da ya bukaci da a sallami tare da bincikar ministan sadarwa Dr. Isa ali pantami Kamar Yadda Wani dan majalisa ya bukata.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2021/04/FB_IMG_1619006224074.jpg?resize=300%2C206&ssl=1)
Tun a farkon wannan watanne cece kuce ya barke kan batun wani murya da aka jiyo ministan nayi addu’a ga wasu mutane.
Lamarin da ya haifar da cece kuce a shafukan sada zumunta dama kasa baki daya.
A yayinda shehin malamin kuma minista ya fito ya bayyana cewa wannan batu da akaji acikin murya na nuna goyan baya ga wasu mutane dake ikirarin jahadi yayi sune a wasu shekaru da yawa da suka shude.
Inda ya bayyana lamarin a matsayin kuriciya.
Lamarin da yasa wasu mutane musamman daga kudancin kasar tura bukatar tsige ministan ga majalisar wakilan kasar