Politics

Yanzu-Yanzu Fintiri ya ci zaɓen gwamnan Adamawa

Yanzu-Yanzu Fintiri ya ci zaɓen gwamnan Adamawa

Hukumar zaɓe a Najeriya ta sanar da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaɓen jihar Adamawa, wanda ya ƙare cikin taƙaddama.

Jami’in sanar da sakamakon zaɓen gwamna na Adamawa, Farfesa Mohammed Mele ya ce Ahmadu Fintiri ya yi nasarar lashe zaɓen ne da ƙuri’a, 430, 861.

Gwamnan mai ci ya samu nasara a kan babbar abokiyar fafatawarsa Aisha Ɗahiru Binani wadda ta samu ƙuri’a, 398, 788.

Wannan nasara ta bai wa Fintiri ikon ci gaba da mulkin jihar Adamawa a wa’adi na biyu.

Da yammacin Talata ne, jami’in sanar da sakamako, Farfesa Mohammed Mele cikin rakiyar wasu manyan jami’an INEC na ƙasa, ya isa zauren karɓar sakamako da ke Yola, inda ya ci gaba da aikin tattara sakamakon ƙananan hukumomin da suka rage.

A ranar 15 ga watan Afrilu ne, hukumar zaɓe ta gudanar da cikon zaɓen cikin wasu rumfuna da ke faɗin ƙananan hukumomin jihar 20.

An sake kaɗa ƙuri’u ne a tashoshin zaɓe 69.

Sakamakon zaɓen da aka ƙarasa ya nuna cewa ‘yar takarar jam’iyyar APC, Aisha Binani ta samu ƙuri’a 6,513, yayin da Gwamna Fintiri na PDP ya samu 9,337.

Zaɓen dai ya gamu da taƙaddama bayan kwamishinan zaɓe na jihar Adamawa Hudu Ari ya sanar da Aisha Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen ba tare da ya fayyace sakamakon kowacce jam’iyya dalla-dalla ba.

Tun da farko a ranar Talata, hukumar zaɓen Najeriya ta ce ta rubuta takarda ga babban sufeton ƴan sanda don ya gudanar da bincike, da nufin duba yiwuwar gurfanar da kwamishinan zaɓen jihar Adamawa da INEC ta dakatar, Barrister Hudu Ari a gaban kotu.

INEC ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya, ya ja hankalin hukumar da ke da alhakin naɗa ma’aikatan zaɓe, game da halayyar kwamishinan zaɓen na Adamawa don ɗaukar mataki.

Babban jami’in INEC, Barrister Hudu Ari, ya shiga zauren tattara sakamakon zabe ne a Yola tare da rakiyar ‘yan sanda da safiyar Lahadi, inda ya ayyana Sanata Aishatu Binani ta APC a matsayin wadda ta lashe zaɓen.

Bai dai yi bayani filla-filla na sakamakon da kowacce jam’iyya ta samu, da kuma yadda aka yi Aisha Binani ta ci zaɓen ba.

Sai dai cikin wata sanarwa da babban jami’inta kan yaɗa labarai da wayar da kan masu zaɓe na ƙasa, Barista Festus Okoye ya fitar, INEC ta ce matakin da kwamishinan zaɓe na jihar Adamawa – REC ya ɗauka na sanar da wanda ya lashe zaɓe haramtacce ne, don haka ta ce ba za a yi amfani da shi ba.

INEC ta kuma ce Hudu Ari ya sanar da sakamakon ne a lokacin da ba a riga an kammala aikin tattara sakamakon zaɓen ba.

Lamarin dai ya janyo ruɗani a Najeriya, inda a Adamawa ‘ya’yan jam’iyyar PDP suka shiga gudanar da zanga-zanga don matsa lamba ga hukumar zaɓe ta kammala aikin sanar da sakamako.

A zaɓen ranar 18 ga watan Maris, INEC ta bayyana gwamna mai ci Ahmadu Umar Fintiri da cewa ya samu ƙuri’a 421,524.

Sai babbar abokiyar fafatawarsa ta jam’iyyar APC, Sanata Aisha Dahiru Binani wadda ta samu ƙuri’a 390,275.

Ita ce mace ta farko da ta taɓa zuwa wannan mataki na zaɓen da aka ƙarasa a takarar gwamna, tun bayan komawar Najeriya mulkin dimokraɗiyya a 1999.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button