![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/03/Capture-2022-03-02-16.03.33.jpg?resize=780%2C470&ssl=1)
YANZU-YANZU: Kwankwaso na daf da sauya sheƙa zuwa NNPP
Tsohon Gwamnan Kano, Rabi’u Kwankwaso na daf da sake barin jam’iyar adawa ta PDP zuwa New Nigeria Peoples Party, NNPP.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/03/FB_IMG_1646233195749.jpg?resize=300%2C296&ssl=1)
Sakataren jam’iyar na ƙasa mai barin gado, Agbo Gilbert Major ne ya fasa ƙwai a kan shirin na Kwankwaso a yayin taron masu ruwa da tsaki na ƙasa da jam’iyar ke shirin yi a Abuja.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa Major ya ce tuni Kwankwaso ya gana da shugabannin jam’iyar domin tsara sauya shekar ta sa zuwa NNPP.
Ya ƙara da cewa yayin da a ke tunkarar kakar zaɓe ta 2023 a kasar nan, akwai bukatar a yi wa jam’iyar NNPP garambawul, inda ya ƙara da cewa ƴan siyasa da dama na kan hanyarsu ta shigowa jam’iyar.
https://youtu.be/947MOgN6TwU