![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/09/dfgimages-55-2.jpeg?resize=696%2C432&ssl=1)
BIDIYO: Masha Allah Saudiyya ta kama mutumin da ya tafi Makka takanas don yi wa Sarauniya Umara
Mahukunta a Saudiyya sun kama wani mutum wanda ya tafi Makka takanas don yin Umara a madadin Sarauniya Elizbeth ta II.
![](https://i0.wp.com/www.arewanewseye.com/wp-content/uploads/2022/09/gghimages-55-4.jpeg?resize=300%2C193&ssl=1)
A ranar Litinin ne mutumin, wanda dan asalin kasar Yemen ne ya wallafa bidiyonsa a babban masallacin Makka yana dawafi.
A cikin bidiyon ya rubuta cewa na sadaukar da Umarar da na yi ga Sarauniya Elizebeth ta II, ya ce yana addu’ar Allah Ya yafe mata kura-kuranta.
An dai yada bidiyon a kafafan sada zumuntar Saudiyya inda mutane suka rinka kira a shafukansu na Tiwita da a kama shi.
Saudiyya ta haramta wa mahajjatan da suke je kasar daukar kwalaye mai dauke da rubuce-rubuce ko kuma ambatar sunan wasu da zummar kamfe ko wani abu dabam.
Yayin da aka amince cewa wani zai iya yi wa mamaci Musulmi Umrah, ba a amince a yi wa wanda ba Musulmi ba kamar Sarauniya, wadda shugaba ce a Cocin Majami’ar Ingila.
Ga Karin Bayani 👇👇👇👇